Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

Ficewa Daga ECOWAS:  Abdulsalami Ya Nemi Nijar, Mali, Burkina Faso Su Koma

Tsohon shugaban kasa kuma ɗaya daga cikin masu shiga tsakani kan rikicin ƙungiyar ECOWAS da jumhuriyar Nijar, Janar Abdulsalami Abubakar mai ritaya, ya yi kira ga ƙasashen yanki uku da su koma cikin ƙungiyar.

Wannan ne karon farko da mai shiga tsakanin ya furta cewa, ficewar Ƙasashen Burkina-Faso da Mali da kuma jumhuriya Nijar daga Ecowas mayar da hannun agogo baya ne.

A cewarsa matakin ƙasashen zai iya kawo naƙasu ga tattalin arzikin yankin.

Janar Abdulsalami Abubakar ya yi kira ga ƙasashen uku da su dawo cikin garke a yi tafiya da su, domin sarkin yawa ya fi sarkin ƙarfi.

Exit mobile version