Home Labaru El-rufa’i Ya Rantsar Da Sabbin Shugabannin Kananan Hukumomi

El-rufa’i Ya Rantsar Da Sabbin Shugabannin Kananan Hukumomi

79
0

Gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufa’i, ya roƙi sabbin shugabannin kananan hukumomi da mutane su ka zaɓa su maida hankali wajen yi wa al’ummar su aikin da su ke bukata.

El-Rufa’i, ya kuma taya sabbin shugabannin murna bisa nasarar da su ka samu a zaben kananan hukumomi da ya gudana a jihar Kaduna.

Gwamnan ya bayyana haka ne, a cikin wani sakon bidiyo da ya wallafa a shafin sa na Facebook, wanda ke kunshe da jawabin sa a wajen rantsar da sabbin shugabannin.

El-Rufa’i, ya kuma gargaɗi sabbin shugabannin kananan hukumomin da cewa, kada su sake su nuna bambanci tsakanin waɗanda su ka zaɓe su da waɗanda ba su zaɓe su ba.