Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

Doka Akan Kayan Abinci Za Ta Kara Jefa ‘Yan Najeriya Cikin Kunci – PDP

Zaben Kogi: PDP Ta Nada Kwamitin Yakin Neman Zaben Gwamnan Jihar

Zaben Kogi: PDP Ta Nada Kwamitin Yakin Neman Zaben Gwamnan Jihar

Jam’iyyar PDP ta ce sabon umarnin da shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya bayar akan janye tallafi akan shigo da kayan abinci bai dace ba.

Jam’iyyar ta ce idan aka yi la’akari da halin kuncin rayuwa da ‘yan Najeriya ke ciki, bai kamata shugaban kasa ya yanke wannan shawarar ba.

A wannan makon ne  shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya ba babban bankin Najeriya CBN umarnin  ya daina bayar da tallafin sauyin kudi ga masu kasuwancin shigo da abinci cikin Najeriya.

Mai  Magana da yawun shugaban kasa Garba Shehu, ya ce shugaban kasa ya bayar da wannan umarni ne domin inganta cinikin kayan abincin da aka noma a cikin gida.

Ya ce gwamnatin tarayya  za ta yi amfani da kudin tallafawa masu shigo da kayan abinci wajen inganta tattalin arziki. Sakataren yada labarai naJam’iyyar PDP Kola Ologbondiyan, ya ce sabon umarnin zai kawo lalacewar ingancin abincin da jama’a za su ke ci, sannan kuma ya kara jefa kasa cikin halin tsanani, bayan wanda ake fama da shi a yanzun.

Exit mobile version