Gwamnatin Tarayya, ta ce mai yiwuwa ta ce dalibai su rubuta jarabawar GCE a cikin watan Nuwamba, matukar aka kasa kammala shirye-shiryen rubuta jarabawar WASSCE, ta Afrika ta Yamma cikin lokacin da aka tsaida.
GCE dai jarabawa ce ta daban, wadda ake rubutawa a cikin watan Nuwamba, kuma a fito da sakamakon ta cikin watan Disamba.
Karamin Ministan Ilmi Emeka Nwajuiba ya bayyana haka, a wajen wani taron manema labarai da ya gudana a kan halin da ake ciki game da cutar Coronavirus a Nijeriya.
Minista ya ce canjin ya zama wajibi, ganin cewa babu wani dalilin da zai sa a kara wa’adin lokacin rubuta jarabawar WASSCE.
You must log in to post a comment.