A kasar China akalla mutane 29 ne suka rasa rayukan su bayan wata zabtarewar kasa yayinda ake ci gaba da neman wasu 22 a wani kauye mai tsaunika dake da nisan kilometa dubu 2 da dari uku da babban birnin kasar.
Kasar China na daga cikin kasashe da lamarin zabtarewar kasa ke janyo mutuwar da dama daga cikin yan kasar.
A shekara ta 2017 kimanin mutane 141 suka bata sakamakon zabtarewar kasa da aka samu a kasar ta China da ya yi sanadiyar birne gidaje sama da 40 tare a wani gari dake lardin Sichuan a kudu maso yammacin kasar.
Al’amarin ya shafi yankin Sichaun, inda rahotanni suka ce zabtarewar ta janyo rusa gidaje da dama.
Gwamnatin kasar ta ware
akala milyan 30 na kudin kasar a matsayin tallafi zuwa masu bincike ,kudin da
za a yi amfani da su domin samarwa mutanen da suka rasa matsugunin wurin zama
na gajeren lokaci.
You must log in to post a comment.