Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

Bikin Rantsar Da Firaminista: Shugaba Buhari Ya Isa Kasar Habasha

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya isa kasar Habasha domin halartar bikin rantsar da firaminista Abiy Ahmed a sabon wa’adi na biyu da zai gudana a yau Litinin.

Wata sanarwa da fadar shugaban kasa ta fitar a ranar Asabar ta ce, shugaba Buhari na daga cikin manyan bakin da za su yi jawabi a bikin rantsar da Abiy Ahmed.

Daga cikin wadanda suka rufa wa shugaba Buhari baya a cewar sanarwar wacce Femi Adesina ya fitar, akwai ministan harkokin wajen Geoffrey Onyeama, da babban daraktan hukumar tattara bayanan sirri Ambasada Ahmed Rufai Abubakar.

A ranar Talata ne dai ake sa ran shugaba Buhari zai dawo gida Najeriya.

Exit mobile version