Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

An Sace Sama Da Mutane 100 Masu Ibada A Wani Coci Da Ke Kaduna

Shugaban kungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen jihar Kaduna Rabaran Joseph John Hayab, ya ce ‘yan bindiga sun sace sama da mutane 100, bayan sun kashe mutum guda a wani hari da su ka kai wani coci a jihar Kaduna.

Rabaran Hayab ya shaida wa manema labarai cewa, lamarin ya faru ne a Cocin Emanuel Baptist da ke ƙauyen Kakau-Daji a wajen garin Kaduna a ranar Lahadin da ta gabata, yayin da mutane ke tsaka da yin ibada.

Gwamnatin jihar Kaduna, ta ce ta na kan tattara wasu bayanai game da sabbin hare-haren da aka ƙara kaiwa bayan na cocin kafin ta fitar da sanarwa gaba ɗaya.

Bayanai sun nuna cewa, lamarin ya faru ne a daidai lokacin da mabiyan ke tsakiyar ibada a cikin cocin, inda maharani su ka safka masu da harbe-harbe.

Exit mobile version