Home Labaru An Fara Binciken Wasu Ministoci Biyu A Kan Almundahanar Hannun Jari

An Fara Binciken Wasu Ministoci Biyu A Kan Almundahanar Hannun Jari

295
0

Rahotanni na cewa, ana zargin tsohon ministan masana’antu da zuba hannun jari Okechukwu Enelamah, da tsohon ministan kasafi Udoma Udo Udoma da laifin taka rawa a wata cuwa-cuwa da ta janyo ‘yan Nijeriya 65,000 su ka yi asarar dala biliyan biyu a bankuna.

Okechukwu Enelamah, Tsohon Ministan Masana’antu Da Zuba Hannun Jari
Okechukwu Enelamah, Tsohon Ministan Masana’antu Da Zuba Hannun Jari

An dai kaddamar da bincike a kan ministocin biyu ne, biyo bayan korafin da aka kai wa Atoni Janar na Nijeriya Abubakar Malami a ranar 3 ga watan Afrilu na shekara ta 2019.

Takardar karar mai taken ‘Almundahana’, ta koka a kan  babakeren dala bilyan biyu da rashin adalci wajen azurta wasu ‘yan kalilan ta hanyar talauta ‘yan Nijeriya 65,000 masu hannun jari a bankuna.

Ana dai zargin ministocin da amfani da kujerun su wajen danne wasu ‘yan Najeriya 65,000 da su ka zabu jari saboda jin dadin wasu masu hannu da shuni.

Leave a Reply