Kungiyar Amnesty International a Nijeriya, ta yi watsi da matsayin da ministan watsa labarai Lai Mohammed ya ɗauka na cewa ba a samu kashe-kashe a zanga-zangar EndSARS da ta faru a Legas ba.
Haka kuma, kungiyar marubuta a kan harkokin kare hakkin bil’adama ta Nijeriya HURRIWA, ta soki lamirin ministan da cewa ba ta san zaman da ya key i a kan kujerar ministan yada labarai a Nijeriya ba.
Kungiyoyin sun ce, yadda ake samun jawaban shugaban kasa da ministan yada labarai suna karo da juna a kan matsayar gwamnati game da lamari mai muhimmanci, hakan zai iya sauya tunanin ‘yan Nijeriya su ki gaskanta duk abin da gwamnati za ta fada nan gaba.

