Home Labaru Kiwon Lafiya Ambaliya: Mutum 49 Sun Mutu A Arewa Maso Yamma- NEMA

Ambaliya: Mutum 49 Sun Mutu A Arewa Maso Yamma- NEMA

207
0
IMG 20240813 WA0021
IMG 20240813 WA0021

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa (NEMA), ta ce akalla mutane 49 ne, suka rasu a Arewa Maso Gabas, a sanadin mamakon ruwan sama da ya haddasa ambaliyar ruwa.

Kakakin hukumar, Manzo Ezekiel ne, ya sanar da hakan cikin wata sanarwa inda ya  bayyana cewa jihohin Adamawa da Taraba na yankin ne da kuma Jigawa lamarin ya fi shafa, inda mutum sama da 41,344 suka rasa matsuguninsu.

Kawo yanzu ambaliyar ta lalata gonalki masu fadin hekta 693 yayin da ake fama da hauhawar farashin kayayyakin abinci.

Leave a Reply