
Shugaban kungiyar Yarabawa ta Afenifere Pa Ayo Adebanjo, ya maida martani a kan ayyana Bola Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaɓen shugaban ƙasa.
Yayin da ya ke jawabi a wata tattaunawa ta wayar tarho da kafar yada labarai ta BBC, Adebanjo ya bayyana zaɓen da ya ba Tinubu nasara a matsayin mai cike da kurakurai.
Ya ce sakamakon zaɓen shugaban ƙasa ba abu ne da za a amince da shi ba, kuma hakan na iya haifar rikici a Nijeriya.
Adebanjo, ya ce gazawar da hukumar zabe ta yi wajen amfani da na’urar BVAS a rumfunan zaɓe kamar yadda ta yi alkawari tun farko, ya nuna cewa wasu sun tsara yadda zaɓen zai gudana da kuma ɗan takarar da su ke so ya yi nasara.
You must log in to post a comment.